News
Tallafin Biliyan 180: Gwamnoni Ba Abin Yadda Bane Da Kuɗaɗe. NLC
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.
Kungiyar Kwadago ta Kasa (NLC) ta soki shirin mika Naira biliyan biyar na tallafi ga gwamnonin jihohi 36 a Najeriya.
Kungiyar ta ce gwamnoni ba abin yarda ba ne inda su ka ce gwamnonin kawai za su ba wa ‘yan siyasa ne a jihohinsu.
A baya dai an sha ba wa gwamnonin jihohi irin wadannan kudade don rabawa talakawa amma kuma su ka mamaye kudin tare da ba wa wasu ‘yan tsiraru da su ke da alaka da su.
A ranar Alhamis 17 ga watan Agusta, Gwamnatin Tarayya ta sanar da ware Naira biliyan biyar ga jihohi 36 na kasar da kuma ware tireloli 180 na shinkafa don rage radadin yunwa.
Gwamnatin Tarayyar ta ware Naira biliyan 180 don rabawa jihohi 36 Naira biliyan biyar don rage radadin cire tallafi.
Tun bayan cire tallafin man fetur da Shugaba Bola Tinubu ya yi, ‘yan kasar su ka shiga mawuyacin hali.
Cire tallafin ya jawo hauhawan farashin kayayyaki da kuma tsadar mai din da ta jefa ‘yan Najeriya cikin wani irin yanayi
Kungiyar NLC a kwanakin baya ta yi zanga-zanga kan hauwawan farashin kaya a kasar da kuma neman Tinubu ya gyara matatun mai a kasar nan.
Wasu da dama na ganin cewa, bai wa gwamnoni irin wadannan kudade zai sanya su raba ma yan jam’iyyar su ne maimakon ainihin masu bukatar tallafin kamar yadda aka sha zargi a baya.
