News
Masu Bukata Ta Musamman Sunyi Barazanar Kai Tinubu Kotu Idan Bai Basu Kujerar Minista Ba
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.
Yayin da ake sa ran shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a ranar Litinin din nan zai rantsar da ministoci da mambobin majalisar ministocinsa
Kungiyar nakasassu,ta Arewacin Najeriya, NNDF, ta yi barazanar daukar matakin shari’a kan shugaban kasa kan rashin sanya su cikin sunayen ministoci da sauransu wajen nade naden da yayi.
An tsinci gawar wata yarinya ‘yar shekara 16 da ta bata a cikin rijiya a Jigawa
Shugaban kungiyar na kasa, Yerima Suleiman a ranar Lahadin da ta gabata ya bayyana aniyar kungiyar na tunkarar kotu, inda ya bayar da misali da wata doka da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sanyawa hannu a shekarar 2018 wadda ta tanadi kashi 5% na duk nade-naden siyasa a bai wa nakasassu.
Suleiman ya ce kungiyar ta yanke shawarar zuwa kotu domin a bi musu hakkinsu.
A cewarsa zamu garzaya kotu domin ta fassara dokar. Dokar ta 2018 da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sanya wa hannu ta tilasta wa nakasassu kashi 5 cikin 100 na mukamai. Don haka ne muka ga ba mu da wani wakili a duk nadin mukamai na siyasa da aka yi kawo yanzu.
Don haka ne muka shirya zuwa kotu domin ta taimaka mana wajen fassara dokar da tsohon shugaban kasar ya yi.
Don haka ba ma goyon bayan bikin rantsar da ministocin da shugaba Tinubu zai yi gobe ba.
Wasu mutane za su so su faɗi haka amma akwai hukumar da aka kafa don kula da nakasassu. Hakan bai shafi kashi 5 cikin 100 na nadin mukamai na siyasa ba kamar yadda doka ta ƙunsa in ji Suleiman.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
