Connect with us

News

Jami’in Hukumar DSS Ya Soka Wa Tsoho Wuka Kan Naira N3,000

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

 

Advertisement

Ana zargin wani jami’in hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ya soka wa wani dattijo mai shekara 62 wuka kan Kudi Naira 3,000.
Rahotanni na nuni da cewa jami’in na DSS ya soka wa mutumin wuka ne saboda taƙaddamar da suka yi kan kuɗin wutar lantarki Naira 3,000.

Darajar Kudin Najeriya Ta Sa Ke Karyewa

Dattijon mai suna Omoshola Oludele, shi ne kiya-tekan gidan da jami’in da DSS ke zaman haya a unguwar Tinumola da ke garin Osogbo, Jihar Osun.

Advertisement

Shaidu sun ce kiya-tekan ya je tattara kuɗin wutan gidan ne, amma jami’in ya ki biya, lamarin da ya kai su ga cacar baki, har jami’in ya caka masa wuka.

Wani ganau mai suna Tosin Moronkola, ya ce jami’in na DSS ya yi wa Mista Oludele mummunan rauni a kwankwaso, kuma an asibiti domin yi masa magani.

Advertisement

Mazauna unguwar sun bukaci ’yan sanda da sauran hukumomin da ke da alhaki su ɗauki mataki a kan jami’in na DSS domin guje wa aukuwar irin haka a nan gaba.

Wani babban jami’in DSS ya shaida wa wakilin jaridar Daily Trust cewa hukumar za ta bincika lamarin kuma za ta hukunta wanda ake zargin idan ta same shi da laifi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending