News
Hatsaniya Ta Kaure Kan Zargin Cirewa Wata Gawa Ido A Asibitin Kwararru Da Ke Gombe
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Hatsaniya Ta Kaure Kan Zargin Cirewa Wata Gawa Ido Daya A Asibitin Kwararru Da Ke Gombe
An samu barkewar yamutsi a asibitin kwararru na tarayya da ke jihar Gombe, biyo bayan zargin cire idon wata mata da ta rasu a asabitin.
Za Mu Tsayar Da Komai Cak A Najeriya Ranar 3 Ga Watan Oktoba – ’Yan Kwadago NLC
LEADERSHIP ta ruwaito cewa, zargin ya auku ne ranar Talata wanda hakan ya hadasa fitowar wasu matasa da mata daga Unguwar Bagadaza, yankin da marigayiyar ta fito, inda suka gudanar da zanga-zanga.
Kazalika, an ruwaito cewa, ‘yansanda da sauran jami’an tsaro sun kawo dauki a gurin, inda suka garkame kofar shiga asibitin domin hana masu zanga-zangar kutsawa cikin asibitin.
Sai dai mahukuntan asibitin sun kyale wasu daga cikin ‘yan uwan marigayiyar sun shiga cikin asibitin da gawar don a yi gwaji.
Wata ‘yar mai rasuwar mai suna, Na’omi Ibrahim, a hirarta da LEADERSHIP ta ce, mahaifiyar ta mai suna, Halima Ibrahim, ta fara rashin lafiyar a ranar Juma’ar da ta gabata, inda aka yi gaggawar kai ta asibitin don a duba lafiyarta.
Ta ce, bayan ta rasu an ajiye gawarta a dakin ajiye gawa na asibitin ind aka dauko a ranar Talata don a bizne ta.
A cewar Na’omi, bayan an bude gawarta don ‘yanu wanta su yi mata ganin karshe sai aka ga an cire idonta na hagu wanda hakan ya sa ta ankarar da ‘yan uwan.
Naomi ta ce, ana yi wa gawar wanka a asibitin an kuma saka gwar a cikin Akwatin gawa na asibitin.
Yanzu haka ana kan bincike don gano ainihin musabbabin faruwar lamarin.
Wani labarin kuma Za Mu Tsayar Da Komai Cak A Najeriya Ranar 3 Ga Watan Oktoba – ’Yan Kwadago NLC
A yayin da ake cigaba da samun cikas wajen balaguro a filin jirgin sama na Murtala Muhammed dake Legas, biyo bayan komawar da kamfanonin jiragen sama na kasashen waje suka yi zuwa sabuwar tashar jiragen sama, gwamnatin tarayya ta gayyaci kamfanonin jiragen sama na kasashen waje zuwa wani taro a yau.
A sakamakon haka, kwamitin da ministan harkokin sufurin jiragen sama, Festus Keyamo ya kafa domin duba rudanin tafiye-tafiye a filin jirgin sama naMurtala Muhammad da kwamitin ministoci zai gana da masu ruwa da tsaki a domin nemo bakin zaren da warware matsalar.
Fasinjojin kasa da kasa da suka tashi daga Najeriya a ranakun Laraba da Alhamis sun makale a biranen Legas da Cairo da Doha da Landan, da sauran wurare bayan da madaurin kaya na jirgi ya lalace a sabon filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Legas, al’amarin da ya tilastawa kamfanonin jiragen sama jinkirtawa tare da soke tashin jirage.
Har yanzu zuwa karshen mako matsalar tafiye-tafiye na ci gaba da wanzuwa inda fasinjojin ke kwashe sa’o’i a kan layi domin tantance su ta hanyar binciken tsaro
