Business
Hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun kakaba dokar hana fitar da Makamashin iskar Gas zuwa kasashen waje
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun kakaba dokar hana fitar da Makamashin iskar Gas zuwa Najeriya da wasu kasashe, kamar yadda yake kunshe cikin wata sanarwa da gwamnatin ta fitar a ranar Talata 3 ga watan Oktoban da muke ciki.
A cewar sanarwar, ya kamata a yi amfani da iskar gas da ake samarwa a cikin gida domin wadata kasuwannin dake jamhuiryar Nijar.
Babban Jojin Najeriya Ya Ce Babu Barazanar Da Zata Hana Alkalai Yin Aiki Da Doka
A cikin shekarun da suka gabata, Nijar na fitar da iskar gas zuwa makwabciyarta Najeriya, kuma kasashen biyu sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna kan shigo da albarkatun man fetur a cikin shekarar 2022.
An sanya hannu kan yarjejeniyar a hukumance a gaban tsohon karamin ministan man fetur na Najeriya, Timipre Sylva da Foumakoye Gado, wanda ya wakilci jamhuriyar Nijar a lokacin.
A wani labarin kuma Babban Jojin Najeriya Ya Ce Babu Barazanar Da Zata Hana Alkalai Yin Aiki Da Doka
Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.
Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.
A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.
Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.
