News
Akalla Mutane 21 Ne Suka Mutum Sanadiyyar Hatsarin Mota Da Ya Afku A Hanyar Kaduna Zuwa Abuja
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Akalla mutane 21 ne suka rasa rayukansu a wani hatsarin mota da ya afku a hanyar Kaduna zuwa Abuja tsakanin kan iyakar jihohin Kaduna da Neja a ranar Alhamis.
Channels tv ta ruwaito cewa hatsarin ya hada da wata babbar mota da wata motar bas da ta nufi Kano daga Abuja da jihar Katsina.
Wata majiya daga hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) a jihar Kaduna, ta bayyana cewa hatsarin ya afku ne sabida lalacewar Hanyar.
lamarin da ya tilastawa duk motocin da suke tahowa daga sassan daban-daban yin tuki ta hanya daya sakamakon kyaran titin. Titin Kaduna zuwa Abuja wanda ya dauki lokaci mai tsawo ba a kammala shi ba .
A cewar jami’in FRSC, nan take direban motar ya gudu daga inda hatsarin ya afku, wanda hakan ya haifar da cunkoson ababen hawa da suka taru a kan babbar hanyar da ta dauki tsawon sa’o’i da dama.
An garzaya da fasinjoji uku da suka tsira zuwa asibitin tunawa da Umaru Musa da ke garin Sabon-Wuse, kusa da kan iyaka tsakanin jihohin Kaduna da Neja domin kula da lafiyarsu, yayin da aka ajiye gawarwakin wadanda suka mutu a dakin ajiyar gawa na asibitin.
