News
Wasu Tsaffin Gwamnonin PDP Tare Nyesom Wike Sun Gana Da Shugaban Kasa
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Ministan Abuja Nyesom Wike ya jagoranci tawagar tsaffin gwamnonin guda hudu da kuma guda daya dake kan mulki a halin yanzu, inda suka gana da shugaban kasa Bola Tinubu a daren jiya.
Rahotanni sun baiyana cewar an fara yin ganawar ne a gidan minista Wike dake Abuja, kafin daga bisani su garzaya wajen shugaban kasa Bola Tinubu a fadarsa dake Villa Abuja.
Duk da cewar babu bayanin abunda ganawar ta kunsa, sai dai wasu rahotanni na baiyana cewar ganawar tasu bata rasa nasaba da inganta alaka tsakanin tsaffin gwamnonin da kuma shugaban kasa.
A wani labarin kuma Kungiyoyin Kwadago Na Kasa Sun Baiwa Gwamnoni Wa’din Mako Biyu Domin Fara Biyan Karin Albashi Na Dubu 35
Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.
Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.
A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.
Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
