Connect with us

News

Kungiyoyin Kwadago Za Su Tsunduma Yajin Aiki A Ranar 14 Ga Nuwamba

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Advertisement

Shugabannin kungiyar kwadago ta Nijeriya NLC da TUC sun sanar da tsunduma yajin aikin gama gari a fadin kasar nan a ranar Talata mai zuwa 14 ga watan Nuwamba 2023.

Shugabannin kungiyoyin biyu, sun cimma wannan matsaya ne bayan wani taron majalisar zartarwar kungiyar ta kasa na musamman da aka yi ranar Talata a Abuja.

Advertisement

Ka canza sana’a, siyasa ba ta karɓe ka ba – Tinubu ya faɗa wa Obi

Matakin da kungiyar kwadagon ta dauka ya biyo bayan cin zarafin da aka yi wa shugaban NLC na kasa, Joe Ajaero a makon da ya gabata a jihar Imo.

 

Advertisement

Kungiyar kwadagon ta zargi kwamishinan ‘yansandan jihar Imo, Mohammed Barde da hannu wajen cin zarafin Ajaero kwanan nan a Owerri, babban birnin jihar Imo.

Kungiyar Kwadago a ranar Juma’ar da ta gabata ta baiwa Gwamnatin Tarayya wa’adin kwanaki biyar domin ta maye gurbin kwamishinan ‘yansandan, yayin da ta kuma zargi Gwamna Hope Uzodimma da ke neman a sake zabensa da harin da aka kai wa Ajaero duk da cewa, Gwamnan ya ce ba shi da hannu kan cin zarafin shugaban kungiyar kwadagon.

Advertisement

 

Kungiyar Kwadagon ta kuma bukaci a kama tare da gurfanar da wasu daga cikin hadiman gwamnan inda ta yi barazanar daukar wani mataki na tsunduma yajin aiki a duk fadin Nijeriya idan ba a aiwatar da bukatunsu ba.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending