News
Kotu Ta Tura Wani Matashi Zuwa Gidan Kurkuku Na Tsawon Watanni 4 Bisa Samunsa Da Laifin Satar Doya
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Wata kotu dake zamanta a Dei-Dei dake Abuja, ta tura wani matashi mai suna Felix Adams zuwa gidan kurkuku har tsawon watanni hudu bisa samunsa da laifin satar doya.
Matashin mai shekaru 22 da ba a bayyana addireshinsa ba, ana tuhumarsa da laifin shiga da kuma aikata laifin sata.
Kotu ta yankewa sojan daya kashe gwani aisami hukuncin kisa ta hanyar RATAYA
Dan sanda mai gabatar da kara Chinedu Ogada, ya bayyanawa kotun cewa wanda ake tuhumar ya aikata laifin ne a ranar 19 ga wata Oktoba 2023.
Ya ce yayin da ‘yan sanda suke gudanar da bincike sun gano cewa matashin ya sace tarin doya ne a wata gona mallakin makarantar sikandiren Dutse Alhaji.
Chinedu, ya kara da cewa wanda ake tuhumar yayi bayani kan cewa ya saci doyar ne da niyyar sayar da ita daga bisani aka kama shi.
Ogada, ya ce wannan laifi da matashin ya aikata ya sabawa sashi na 348 da 287 na kundin hukunce hukuncen penal code. Alkalin kotun, ya gargadi wanda ake tuhumar da ya kasance mai kyakkyawan hali nan gaba bayan kammala zaman gidan gyaran halin.
A wani labarin kuma Kotu ta yankewa sojan daya kashe gwani aisami hukuncin kisa ta hanyar RATAYA
Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ta jaddada cewa babu wani wuri Falasɗinawa za su iya zuwa don ɓuya daga hare-haren Isra’ila a Zirin Gaza.
“Mun faɗa mun sake faɗa,” in ji hukumar kula da ‘yan gudun hijirar Falasɗinawa ta UNRWA cikin wani saƙo a dandalin X. “Muna sake faɗa, babu wani gidan ɓuya a Gaza.”
Ta ƙara da cewa: “Wahalar da ɗana’dam ke sha kai ba zai ɗauka ba. Cigaba da kai hare-hare da kuma faɗaɗa su zuwa kudancin Gaza na ƙara maimaita bala’in da aka fuskanta a ‘yan makonnin da suka wuce.”
UNRWA na wannan magana ne yayin da rundunar sojin Isra’ila ta ce dakarunta na kai samame a tsakiyar biranen Gaza uku, ciki har da Khan Younis – birni mafi grima a kudancin Gaza.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
