News
Mayakan Boko Haram Sun Kashe Hafsan Soji Sun Kwace Sansanin Sojoji A Borno
DAGA UMAR IBRAHIM HOTORO
Mayakan Boko Haram sun kashe wani hafsan soja da wasu ’yan sa-kai biyu a wani ƙazamin hari a sansanin sojoji a Jihar Borno.
Wata majiyar soji ta shaida Jaridar Aminiya cewa an kasa ɗauko gawar waɗanda aka kashe, saboda tsananin faɗan da aka gwabza da misalin ƙarfe 1 na dare a sansanin da ke yankin Krenowa a Ƙaramar Hukumar Marte ranar Asabar.
AFCON 2023: Ghana Ta Kori Koci Da ’Yan Tawagar Horas Da ’Yan Wasanta Bayan Cire Su
Ta ƙara da cewa maharan sun lalata wata motar yaƙi, amma direbanta ya tsira da rauni a ƙafarsa, sannan sojoji fiye da 100 tare da makamai da sauran kayan aikinsu sun janye zuwa garin Marte.
Ƙoƙarinmu na jin ta bakin kakakin Hedikwatar Tsaro ta Ƙasa, Manjo-Janar Edward Buba, ya faskara.
Mun kira wayarsa amma ba ta shiga, sannan har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoton ba mu samu amsar rubutaccen saƙon da aka tura masa ba.
Amma wasu majiyoyi sun shaida mana cewa mayaƙan Boko Haram sun kai wa sojojin hari ne kwanaki biyar bayan sojojin sun ƙwace sansanin ƙungiyar da ke Krenowa a ƙoƙarin sojojin na kakkaɓe ’yan ta’adda.
Wani soja ya shaida wa wakilinmu cewa, “mun kai musu hari muka ƙwace sansaninsu, amma daga baya suka kawo mana harin kwanton ɓauna, dole muka janye.
“Ina kyautata zaton ɓuya suka yi, saboda babu wata alamar shirin harin kwanton ɓauna.
“A ƙarshe dai sansanin rundunar 27 Task Force da ke garin Marte muka koma,” in ji majiyar sojin.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
