Connect with us

News

NSCDC Ta Kori Jami’inta Da Ake Zargi Da Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Zamfara

Published

on

NSCDC Ta Kori Jami’inta Da Ake Zargi Da Hada Baki Da ‘Yan Bindiga Wajan Saffar  Kwayoyi Da Harsasai A Zamfara

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

Hukumar tsaro na Sibul Difens (NSCDC), reshen jihar Zamfara, ta kori wani jami’in ta, Maikano Sarkin-Tasha, bisa zargin hada baki da ‘yan bindiga wajen samar musu da muggan kwayoyi da harsasai.

Advertisement

Kwamandan rundunar, Sani Mustapha ne ya bayyana hakan a ranar Asabar yayin da yake ganawa da manema labarai a Gusau.

Osasuna ta lallasa Barcelona da ci 4 da 2

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara a ranar Juma’a ta gabatar da wasu mutane 17 da ake zargi da hada baki da ‘yan bindiga ciki har da Sarkin-Tasha.

Advertisement

Mustapha ya ce rundunar ba ta ji daɗin samun labarin damke jami’in ta da ake zargi da hannu dumu-dumu wajen mu’amula da ƴan bindiga ba.

“A bisa bincikenmu na farko, an kama jami’in ne a wani shingen bincike, tsakanin Damba da Sabon Gida, a lokacin da yake kan hanyarsa ta zuwa kauyen Mada da ke karamar hukumar Gusau.

Advertisement

“An same shi da wasu abubuwa da ake zargin wiwi ne da wasu muggan kwayoyi.

“Sauran kayayyakin da aka samu a jikin sa sun hada da sulke guda uku na G3 da sulke guda daya na harba roka.

Advertisement

Mustapha ya ce wannan ba ɗabi’a ba ce ta jami’an rundunar a Zamfara. Daga nan sai ya kara da cewa rundunar za ta ci gaba da saka ɗa’a da kishin kasa a zukatan jami’anta.

 

Advertisement

 

Premium Times

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending