News
Mahaifin Da Ake Zargin Ya Kashe Jiririnsa Ɗan Kwana 3 Ya Shiga Hannun Ƴansanda
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Rundunar ‘Yansandan Jihar Adamawa ta kama Aliyu Yaro, matashi mai shekara 19, bisa zargin kashe jaririnsa ɗan kwanaki uku da haihuwa.
Yaro, mazaunin unguwar Kwacham a Mubi ta Arewa, ya amsa laifin kuma ya jagoranci Ƴansanda zuwa wurin da aka binne jaririn.
Hukumar JSC Ta Kano Ta Dauki Matakin Ladabtarwa Kan Ma’aikatan Shari’a Guda Takwas
LEADERSHIP HAUSA ta ruwaito cewa, Yaro ya aikata wannan aika-aikar ne bayan mahaifiyar jaririn, ta nemi ya ɗauki nauyin kulawa da shi. Yaro ya je gidan mahaifiyar jaririn da daddare, ya tura ta tafi nemo ruwa, sannan ya ɗauke jaririn daga baya ya binne shi a yankin Girpata a Mubi.
Kwamishinan Ƴansandan Jihar, CP Morris Dankombo, ya nuna damuwarsa kan wannan lamari, tare da bayar da umarnin miƙa lamarin zuwa Sashen binciken manyan laifuka don ci gaba da bincike da kuma gurfanar da wanda ake zargin gaban Kuliya.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
