News
Ƙudurin Zaɓe Daga Ƙetare Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisar Wakilai
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Ƙudirin da zai yi wa kundin tsarin mulkin Najeriya kwaskwarima domin bai wa ƴan ƙasar mazauna ƙasashen waje damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓe ya tsallake karatu na biyu a majalisar wakilai a ranar Laraba.
Ƙudirin wanda shugaban majalisar, Abbas Tajudeen da Sodeeq Abdullahi suka ɗauki nauyinsa, na neman yin gyara ga dokar zaɓe ta 2022 domin a bayar da dama ga ƴan Najeriya mazauna ƙasashen waje su kaɗa ƙuri’a.
Abba Hikima Ya Maka Wike Da Wasu Mutane 5 A Kotu Tare da Neman Diyyar ₦500 Miliyan
An amince da karanta ƙudurin karo na biyu a watan Yuli, kuma an miƙa shi ga kwamitin da ke kula da harkokin zaɓe don ci gaba da nazarinsa.
Sai dai bayan tsallake karatu na biyu a ranar Talata, an miƙa shi ga kwamitin gyaran kundin tsarin mulki don ci gaba tattaunawa a kansa.
