News
Pakistan Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Yayin Da Rikici Da Indiya Ke Kara Tsananta
Pakistan ta ce ta yi nasarar gwajin wani sabon makami mai linzami a daidai lokacin da ake fama da karin rashin jituwa tsakaninta da makwabciyarta Indiya.
Rundunar sojin kasar ta ce makamin linzamin ya yi tafiyar kusan kilomita 450 daga inda aka harba shi, kuma gwajin wani bangare ne na aikin tabbatar da lafiyar makamansu da kuma ingancin aikin sojin kasar.
2027: Ana Zargin Wike Da Gwamnonin PDP Sun Cimma Yarjejeniya
Gwamnatin Islamabad ta ce wannan mataki ne da ke nuna shirin dakarunta wajen kare iyakokin kasar da kuma nuna karfi a lokacin da ake fama da kalubale a yankin.
Gwajin ya biyo bayan wani hari da ya kashe ’yan yawon bude ido na Indiya a garin Pahalgam da ke yankin Kashmir a ranar 22 ga watan jiya.
Indiya ta dora laifin kisan kan Pakistan, zargin da ita kuwa Pakistan ta musanta, tana mai cewa ba ta da hannu a lamarin.
Har yanzu ba a ji wani martani daga bangaren Indiya game da harba makamin ba.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
