Connect with us

News

’Yan Bindiga Sun Yi Ajalin Sarkin Shuwaka Bayan Garkuwa Da Shi A Filato

Published

on

’Yan bindiga sun kashe Sarkin Shuwaka na Garga, a karamar hukumar Kanam ta Jihar Filato, Malam Hudu Barau, kwanaki shida bayan sun yi garkuwa da shi. An gano gawarsa a cikin dajin Wanka.

Kungiyar Cigaban Kanam (KADA) ce ta tabbatar da lamarin a cikin wata sanarwa da shugabanta, Shehu Kanam, da sakataren ta, Barrister Garba Aliyu, suka fitar a ranar Litinin. Kungiyar ta bayyana lamarin a matsayin abin bakin ciki da kuma tunatarwa kan yadda matsalar tsaro ta yi kamari a yankin.

Advertisement

Sai Ka Kalli Tallace-Tallace Kafin Ka Samu Takardar Bayan Gida A China

KADA ta soki gwamnati a matakai daban-daban da cewa ta kasa daukar matakan gaggawa duk da rokon da al’umma ke ta yi na kawo karshen hare-hare, garkuwa da mutane da kisan gilla. Ta ce jama’ar Garga da makwabtansu na rayuwa cikin fargaba.

Kungiyar ta yi kira ga Gwamna Caleb Mutfwang da ya ayyana dokar ta baci a yankin tare da tura jami’an tsaro yadda ya kamata.

Advertisement

Haka kuma ta zargi wakilan majalisar jiha da na tarayya daga yankin da gazawa wajen kare jama’arsu daga hare-haren ’yan bindiga.

 

Advertisement

 

LEADSHIP

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending