News
An dage bude makarantu a Sudan saboda ambaliya
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Gwamnatin Sudan ta sanar da dage bude makarantu a fadin kasar, saboda ambaliya da ta daidaita yankuna da dama a kasar.
Da ma a wannan watan ya kamata a fara sabon zangon karatu a kasar, to amma yanzu an dage batun komawar har sai ranar 2 ga watan Oktoba, kamar yadda jaridun cikin gida suka ambato Ministan Ilimi Sir al-Khatim al-Huri yana fada.
Gwamnonin Arewacin Najeriya na so a kafa rundunar ‘yan sandan jihohi
Akalla makarantu 623 ne ambaliyar ta shafa, kuma an dauki matakin ne da nufin gyara su kafin a cigaba da karatu.
Ruwan sama mai karfi da ambaliya sun kashe sama da mutum 100, tare da lalata dubban gidaje a gwamman jihohin Sudan a makonnin da suka wuce.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
