Connect with us

News

Gobara Ta Tashi A Hedikwatar Hukumar NYSC Da Ke Abuja

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

 

 

An samu tashin gobara a hedikwatar hukumar masu yi wa kasa hidima dake birnin tarayya Abuja ranar Juma’a.

 

Advertisement

Hukumar ta ce ba a samu asarar rai ba sakamakon barkewar gobarar kwatsam domin ta takaita ne a hawa na uku na ginin bene mai hawa shida.

 

Takarar Gwamnan Kaduna: Kotu Ta Kori Karar Sani Sha’aban

 

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan hulda da manema labarai, Eddy Megwa, ya fitar ranar Juma’a.

 

Advertisement

Ya ce nan take ofishin babban birnin tarayya da na hukumar kashe gobara ta tarayya suka kashe gobarar a lokacin da lamarin ya faru da misalin karfe 07:30 na safe.

 

Megwa ya kuma ce benen da abin ya shafa na cikin tsare-tsare, bincike da kididdiga da kuma babban ma’aikata inda gobarar ta shafi wani daki ne kawai da na’urorin lantarki.

 

Ya ce, “An yi sa’a, ba a yi asarar rai ba kuma an kwashe dukkan muhimman takardu da gaggawa kuma an kiyaye su.

 

Advertisement

“Masu gudanar da shirin suna godiya sosai ga Ma’aikatar kashe gobara ta Tarayya da FCT saboda yadda suka mayar da martani cikin gaggawa wanda ya rage tasirin lamarin.

 

“Hukumar ta kuma yaba wa dukkan hukumomin tsaro bisa gagarimar rawar da suka taka a lokacin da lamarin ya faru.”

 

 

NAN

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending