Connect with us

News

Cutar Mashako ta kashe yara hudu a Kano

Published

on

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA 

 

Advertisement

An samu bullar cutar Mashako yayin da  ta kashe yara hudu a kauyukan karamar hukumar Mingibir ta jihar Kano.

Wata sanarwa da jami’in yada labarai na karamar hukumar Tasiu Yahaya Dadin-Duniya ya fitar, wanda aka turawa da gidan rediyon Arewa.

Advertisement

Hukumar EFCC Ta Sake Gurfanar Da Tsohon Gwamna, Dansa Bisa Zargin Almundahanar Naira Biliyan 29 A Gaban Kotu

A cewar sanarwar “Yara hudu ne suka mutu sakamakon cutar Mashako sannan kuma yara 28 sun kamu da cutar a kauyukan Kwarkiya, Kuru, Kunya da Minjibir dake karamar hukumar Minjibir ta jihar Kano.

“Jami’in riko na karamar hukumar, Muhammad Yakubu Kunya, ya yi kira ga hukumomi da masu ruwa da tsaki da su gaggauta kai wa karamar hukumar Minjibir dauki domin kare lafiyar al’umma”.

Advertisement

Sanarwar ta ce Hakimin Karamar Hukumar ya kuma bukaci sarakunan gargajiya da malaman addinin Islama a cikin al’umma da su tashi tsaye wajen wayar da kan al’umma tare da yin addu’ar samun sauki.

A halin da ake ciki, ma’aikatar lafiya ta jihar ba ta tabbatar ko musanta bullar cutar ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending