Connect with us

News

 NLC Ta Umurci Mambobinta Da Su Tsunduma Yajin Aiki A Duk Jihar Da Aka Ki Biyan Mafi Karancin Albashi  

Published

on

NLC ta umurci mambobinta da su tsunduma yajin aiki a duk jihar da aka ki biyanmatsayin mafi karancin albashi

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

Kungiyar Kwadago ta NLC a Najeriya ta umurci ya’yanta da su tsunduma yajin aiki a duk jihar da aka ki biyan N70,000 a matsayin mafi karancin albashi daga ranar 1 ga watan Disamba 2024

Wannan umarnin ya biyo bayan kudurorin da kungiyar NLC ta gudanar a taron majalisar zartarwa ta kasa a karshen mako.

Yadda Kanawa Suka Fara Jingine Motocinsu Suna Rungumar Babur Mai Caji Da Tafiyar Ƙafa Saboda Tsadar Man Fetur

Kungiyar ta lura da jinkiri da kuma kin amincewa da wasu gwamnatocin jihohi suka yi na aiwatar da dokar mafi karancin albashi ta kasa ta shakarar 2024.

Wannan rashin mutunta doka ne da kuma rayukan miliyoyin ma’aikatan Najeriya

Haka zalika Kungiyar ta kuduri aniyar kafa kwamitin aiwatar da mafi karancin albashi na kasa wanda zai fara aikin tantancewa, wayar da wayar da kan jama’a a fadin kasar nan.

Advertisement

“Don haka, an umurci mambobinta da su tsunduma yajin aiki a duk jihar da aka ki biyan N70,000 a matsayin mafi karancin albashi daga ranar 1 ga watan Disamba 2024

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending