Connect with us

News

Gwamnoni Sun Goyi Bayan Kudurin Dokar Harajin Shugaba Tinubu

Published

on

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA 

Kungiyar Gwamnonin Najeriya ta amince da Kudirin Gyaran Haraji, inda ta ba da shawarar cewa kada a kara harajin VAT kuma ta gabatar da muhimman shawarwari.

Advertisement

”Kungiyar ta amince da sabon tsarin raba kuɗin Harajin (VAT) domin tabbatar da daidaiton rarraba arzikin kasa kamar haka :

Kotu Ta Yanke Wa Wasu ‘Yan Mata 3 Hukuncin Kisa

Kashi 50% bisa daidaito,

Advertisement

 

30% bisa la’akari da abin da aka samar,

Advertisement

 

20% bisa yawan jama’a.

Advertisement

 

”Mambobin sun amince cewa bai kamata a kara harajin VAT ba ko rage Harajin Kuɗin Shiga na Kamfanoni (CIT) a wannan lokaci, don kiyaye daidaiton tattalin arziki. Kungiyar ta nemi a ci gaba da ware kayan masarufi da kayan noma daga harajin VAT don kare walwalar ‘yan ƙasa da ƙarfafa aikin gona.

Advertisement

”Taron ya bayar da shawarar cewa bai kamata a saka sharadin kawo ƙarshen wa’adin TETFUND, NASENI, da NITDA a cikin rabon kudaden cigaba a kudirin dokar ba.

”Taron ya goyi bayan ci gaba da aikin majalisa a Majalisar Dokoki ta Kasa wanda zai kai ga kammala amincewa da Kudirin Gyaran Haraji”,

Advertisement

Acewar AbdulRahman AbdulRazaq, Shugaban Kungiyar Gwamnonin Najeriya

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending