Connect with us

News

Wata Babbar Mota Ta Yi Ajalin Mutum 3, Ta Jikkata 40 A Yobe

Published

on

IMG 20260121 WA0006 750x750

Mutane uku sun mutu, yayin da kimanin mutum 40 suka jikkata, sakamakon wani mummunan hatsarin mota da ya faru a kan babbar hanyar Gombe zuwa Potiskum, a Jihar Yobe, arewacin Najeriya.

Lamarin ya auku ne da misalin karfe 2:30 na rana a ranar Laraba, kusa da garin Badejo, a ƙaramar hukumar Potiskum, bayan da wata babbar mota ɗauke da kaya ta ƙwace daga hannun direbanta ta afka cikin mutanen da ke zaune a gefen hanya.

Advertisement

Matakan Da Gwamna Abba Ya Ɗauka Kan Kisan Gillar Mata Da ‘Ya’yanta 6 A Kano

Wasu shaidu sun shaida wa LEADSHIP cewa, motar na tafiya ne da gudu mai yawa, lamarin da ya sa direban ya kasa sarrafa ta, ta kuma yi kan mutane da dama.

Advertisement

Kwamandan Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC) reshen Jihar Yobe, Paul Andrew, ya tabbatar da faruwar hatsarin, inda ya ce an kai waɗanda suka jikkata zuwa asibitoci domin samun kulawa.

A cewarsa, binciken farko ya nuna cewa cunkoson kaya fiye da ƙa’ida da kuma gudu mara misali na daga cikin abubuwan da suka haddasa hatsarin.

Advertisement

Hukumar FRSC ta sake jan hankalin direbobi da su riƙa bin dokokin hanya, musamman direbobin manyan motoci, domin rage yawaitar hatsurran da ke hallaka rayukan jama’a.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending