Connect with us

News

Sanata Gobir Ya Zama Sabon Shugaban Masu Rinjaye A Majalisar Dattawa

Published

on

 

 

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

 

 

Shugabancin jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Adamu, ya zabi Sanata Ibrahim Gobir mai wakiltar Sokoto ta Gabas a matsayin sabon Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Dattawa.

Advertisement

 

Matakin na jam’iyyar na kunshe ne a cikin wata wasika da ta aike wa Shugaban Majalisar, Sanata Ahmed Lawan, mai dauke da sa hannun shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Adamu.

Buhari Yaba Da Umarnin Fito Da Jirage Don Fara Sufuri A Kamfanin Nigerian Air

 

Sanata Ahmad Lawan ne ya karanta wasikar a farkon zaman majalisar na ranar Laraba.

 

Advertisement

Gobir ya maye gurbin tsohon Shugaban Masu Rinjaye a Majalisar, Yahaya Abdullahi, daga (Kebbi ta Arewa), wanda ya sauya sheka zuwa PDP.

 

Kafin nadin nasa, Sanata Gobir ya jagoranci Kwamitin Tsaro da Leken Asiri na Majalisar.

 

Wasikar ta ce, “Dangane da wasikarka mai lamba: NASS9thS/SP/D/12/ mai dauke da kwanan wata 16 ga watan Yunin 2022, inda ka sanar da majalisa zabin jam’iyyarmu a majalisar dattawa.

 

Advertisement

“Ka yarda da wannan nadin da jam’iyyar ta yi wa Sanata Ibrahim Gobir a matsayin wanda zai maye gurbin tsohon Shugaban Masu Rinjaye a majalisar.

 

“Ina na gode muku kan yadda kuke ba mu hadin kai.”

 

AMINIYA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending