Connect with us

News

Har Yanzu Akwai Makarantun Sakandare 75 Da Ke Rufe A Zamfara

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADINNI

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Gwamnatin jihar Zamfara ta ce har yanzu akwai makarantun sakandare akalla guda 75 da suka shafe kusan shekara daya a rufe saboda matsalar tsaro.

Advertisement

 

Babban Sakatare a Ma’aikatar Ilimi ta jihar, Alhaji Kabiru Attahiru ne ya sanar da hakan a Gusau, babban birnin jihar ranar Asabar.

Advertisement

Minista Ya Bukaci A Kammala Aikin Titin Kano Zuwa Kaduna Nan Da Wata 4

 

Advertisement

Yana jawabi ne yayin wani taron kwana biyu kan Manufar Ilimin ’Ya’ya Mata ta Kasa (NPGE) da aka gudanar a jihar.

 

Advertisement

Hukumar Kula da Ilimin Bai-daya ta Jihar (SUBEB) tare da Asusun Tallafa wa Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ne suka shirya taron.

 

Advertisement

Babban Sakataren ya lura cewa galibin makarantun da lamarin ya shafa na ’yan mata ne wadanda aka rufe tun a watan Satumban bara, bayan hare-hare har guda biyu da aka kai wa makarantun ’yan matan a jihar.

 

Advertisement

Sai dai ya ce gwamnatin jihar na ta aiki ba dare ba rana wajen ganin ta sake bude makarantun da aka rufe kusan shekara guda bayan barazanar ’yan ta’adda.

 

Advertisement

Gwamnatin jihar dai ta ba da umarnin rufe ilahirin makarantun jihar ne bayan sace dalibai 75 a makarantar sakandaren gwamnati da ke garin Kaya a karamar hukumar Maradun ta jihar.

 

Advertisement

(NAN)

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending