News
’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 4 A Kaduna
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
’Yan bindiga sun kashe mutum hudu ciki har da wani sabon malamin makaranta da aka dauka aiki a Karamar Hukumar Kajuru ta Jihar Kaduna.
Aminiya ta samu cewa lamarin ya faru ne a wasu kauyuka biyu – Gefe da Tudun Mare – na Karamar Hukumar.
Harin da aka kai a Gefe ya yi sanadiyar mutuwar mutane uku ciki har da shugaban matasan kauyen a daren ranar Lahadi.
Bayanai sun ce harin na biyu ya faru ne a Tudun Mare da ke Maraban Kajuru, inda aka kashe malamin makarantar mai suna Elisha Arziki.
Wani mazaunin yankin mai suna Bilyaminu ya ce an birne shugaban matasan da mutanen kauyen biyu a ranar Litinin.
“’Yan bindigar sun kashe shugaban matasan kauyen da wasu mutum biyu a lokacin da suka kai farmaki kauyen ranar Lahadi.
“An yi jana’izarsu a ranar Litinin yayin da kuma ‘yan bindigar suka kashe wani malami a kauyen Tudun Mare a daren ranar Litinin,” in ji shi.
Kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mohammed Jalige, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya yi alkawarin yin karin haske da zarar ya samu cikakken bayani.
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
