Connect with us

News

Gwamnan PDP Ya Gayyaci Shugaban Kasa Buhari Kaddamar Da Ayyukansa

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Gwamnan Benuwai, Samuel Ortom, ya gayyaci Shugaban Kasa Muhammadu Buhari domin kaddamar da wasu sabbin gine-gine a Gidan Gyaran Hali na Makurdi da ke jiharsa.

 

Advertisement

Gwamna Ortom ya bayyana hakan ne a wani taro da al’ummar Ugondo, yankin da gidan gyaran halin yake.

Dan Dambe Ya Mutu Bayan An Yi Masa Mahangurba

 

Advertisement

Idan dai za a iya tunawa, Gwamna Ortom ya sha sukar gwamnatin shugaba Buhari ta jam’iyyar APC, musamman ma dangane da hare-haren makiyaya a sassan Jihar Benuwai, wadanda suka yi sanadin rasa rayuka da lalata dukiyoyi masu tarin yawa.

 

Advertisement

Gayyatar Ortom ga Buhari na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnan ke tsaka da takun saka da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyarsa ta PDP, Atiku Abubakar, kan zaman Iyorchia Ayu a matsayin shugaban jam’iyyar na kasa.

 

Advertisement

Ortom, na daga cikin gwamoni biyar na PDP da ake kira ‘G-5’ wadanda suka sanya yin murabus Ayu ya yi a matsayin sharadinsu na mara wa Atiku baya a zaben 2023.

 

Advertisement

An fara aikin gyara gidajen yarin ne bayan wasu hare-hare da aka fasa wasu gidajen yari a sassan kasar nan, ciki har da na Kuje da ke Babban Birnin Tarayya Abuja.

 

Advertisement

Ortom ya gargadi al’umma game da yin katsalandan a filin da aka bayar ga ma’aikata da duk wata hukumar tarayya da ke bayar da gudunmawar cigaban al’ummar Benuwai da kuma tsaron lafiyarsu.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending