Connect with us

News

Dalibin Jami’ar Gombe Ya Rasu Yana Tsaka Da Rubuta Jarrabawar Karshe

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

Wani dalibin Jami’ar Jihar Gombe da ke zangon karatu na karshe mai suna Abubakar Muhammad, ya rasu yayin da yake tsaka da rubuta jarrabawar kammala makarantar.

Dalibin dai na karatu ne a sashen koyon aikin Akanta na jami’ar.

Advertisement

Mutum 38 Sun Mutu, Yayin Da Wasu 40 Suka Jikkata A Hatsarin Mota A Yobe

Wani abokin karatun marigayin ya bayyanawa jaridar Aminiya cewa marigayin ya zo dakin rubuta jarrabawa a ranar sai rashin lafiya ta kama shi inda nan take aka garzaya da shi zuwa cibiyar lafiya ta jami’ar dan duba lafiyarsa.

Mutum 38 Sun Mutu, Yayin Da Wasu 40 Suka Jikkata A Hatsarin Mota A Yobe

Sai dai a cewar majiyar, jikin dalibin ya tsananta, amma kafin nan rai ya yi halinsa, inda aka wuce da shi dakin adana gawarwaki a asibiti.

Advertisement

 

 

Advertisement

“Ya rasu a cibiyar lafiya ta jami’ar sannan daga bisani mataimakin shugaban sashen tsaro na jami’ar ya jagoranci daukar gawar zuwa dakin adana gawarwaki na asibitin kwararru na Jihar Gombe tare da wasu abokansa da kuma wasu jami’an jami’ar,” in ji dalibin.

Da wakilinmu ya tuntubi jami’in hulda da jama’a na jami’ar, Mohammed Abubakar, ya tabbatar da rasuwar dalibin.

Advertisement

Sai dai ya ce dama dalibin ba shi da lafiya a ranar tun kafin shigarsa dakin

zana jarrabawar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending