News
Shugaba Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci
DAGA UMAR IBRAHIM HOTORO
Kwamitin shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu a kan sake yi wa tsarin karbar haraji kwaskwarima a kasar nan, ya bayyana cewea, a halin yana tattaunawa da gwamnanonin jihohin tarayyar Nijeriya don cimma yarjejeniyar da zai kai ga janye karbar wasu kananan haraji da ake dorawa kayan abinci da ake zirga-zirga da su tsakanin yankin arewa da kudancin Nijeriya.
Kamitin ya ce, tattaunawar zai kai ga dakatar da harajin da gwamantin jihoji da na kananan hukumomi suke yi, wanda yana takurawa masu safarar kayan abinci a tsakanin jihohin tarayyar Nijeriya.
Yan Kwankwasiyya sun maida Ganduje abin zolaya, bayan ya nemi Abba Gida-gida ya shiga APC
Shugaban kwamitin, Taiwo Oyedele, ya bayyana haka a tattunawarsa da gidan talabijin na ‘Channels’ inda ya yi bayani a kan irin ci gaban da kwamitin ke samu a aikinsa na samar da wani tsari na musanmman ga yanayin karbar haraji a Nijeriya.
Shugaban kasa Bola Tinubu ya kaddamar da akwamitin watanni kadan bayan ranstar da shi a kan karagar mulki, inda aka dorawa kwamitin samar da ingantacciyar tsarin da zai bunkasa yanayin karbar haraji a kasa ya kuma kai ga bunkasar tattalin arzikin Nijeriya.
A tattauanwar, Oyedele ya ce, irin wadanna kananan harajin basa karawa tattalin arziki komai sai dai takurawa al’umma. Ya yi korafin cewa yawancin harajin da ake dorawa kayan abinci da ke zirga-zirga da su daga kudancin zuwa arewacin kasar nan suna takurawa al’ummar Nijeriya kwarai da gaske.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
