Connect with us

News

Kotun Koli Ta Sanar Da Ranar Da Alkalin Alkalan Najeriya Zai Yi Ritaya

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Kotun koli ta sanar da cewa Olukayode Ariwoola zai yi ritaya a matsayin Alkalin Alkalan Najeriya a ranar 22 ga watan Agusta.

Advertisement

A wata sanarwa da aka fitar a ranar Litinin, Festus Akande mai magana da yawun kotun koli ya ce za a gudanar da zaman kotun na ban kwana domin girmamawa ga alkalin alkalan wanda ke cika shekaru 70 na ritaya.

Zanga-zanga: Gwamnati ta fara sayar da buhun shinkafa N40,000

Akande ya kuma ce kotun kolin ta fara hutun ta na shekara a ranar 22 ga watan Yuli inda za ta dawo a ranar 23 ga watan Satumba na 2024 kamar yanda Jaridar DAILY NIGERIAN ta ruwaito

Advertisement

“Shekarar aiki ta 2023/2024 ta zo karshe a ranar Juma’a 19 ga watan Yuli na 2024″, inji sanarwar.

” Kotu ta fara hutu a ranar Litinin 22 ga watan Yuli na 2024 kuma za ta dawo a ranar 23 ga watan Satumba na 2024.”

Advertisement

A ranar 12 ga watan Oktoba na 2022 ne dai tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya rantsar da Ariwoola a matsayin alkalin alkalan Najeriya wata 4 bayan ajiye aikin da Ibrahim Muhammad ya yi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending