Connect with us

News

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Sanata Monday Okpebholo A Matsayin Sahihin Gwamnan Edo.

Published

on

FB IMG 1752146119020

Kotun Ƙoli ta tabbatar Da Sanata Monday Okpebholo a matsayin sahihin Gwamnan Jihar Edo.

Kotun ta yanke hukuncinta ne a ranar Alhamis, inda ta kawo ƙarshen shari’ar da aka dinga yi bayan zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar a ranar 21 ga watan Satumban 2024.

Advertisement

Attajiran Afrika 4 ne ke riƙe da fiye da rabin arziƙin nahiyar   —Oxfam

Kwamitin alƙalai biyar ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Mohammed Garba, ya ce ƙarar da Asue Ighodalo na jam’iyyar PDP ya shigar ba ta da ƙarfi, don haka kotun ta yi watsi da ita.

Mai Shari’a Garba, ya bayyana cewa PDP da ɗan takararta ba su kawo wata hujja mai ƙarfi da za ta nuna cewa Okpebholo bai lashe zaɓen bisa ƙa’ida ba.

Advertisement

Haka kuma ba su nuna yadda hukuncin kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓe da na kotun ɗaukaka ƙara ya saɓa doka ba.

“Mun yi watsi da ƙarar saboda babu ingantacciyar hujja a cikinta. Kotun ta tabbatar da hukuncin da kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓe da kotun ɗaukaka ƙara suka yanke,” in ji Mai Shari’a Garba.

Advertisement

Wannan hukunci ya tabbatar da cewa Sanata Okpebholo na jam’iyyar APC ne, halastaccen wanda ya lashe zaɓen gwamnan Jihar Edo na shekarar 2024.

PDP ta zargi cewa an yi maguɗi a zaɓen, inda ta nemi a soke sakamakon.

Advertisement

Amma kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓe da kotun ɗaukaka ƙara suka yi watsi da ƙorafinta, wanda ya sa suka kai ƙarar zuwa Kotun Ƙoli.

Da wannan hukunci, an rufe duk wata shari’a da ta shafi zaɓen gwamnan Jihar Edo.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

LEADSHIP

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending