Connect with us

News

’Yan Bindiga Sun Sace Gomman Fasinjojin Jirgin Kasa A Edo

Published

on

DAGA MARYAM BASHIR MUSA

 

Advertisement

 

Wasu ’yan bindiga sun yi awon gaba da fasinjoji da dama a wata tashar jirgin kasa da ke karamar hukumar Igueben a Jihar Edo.

Advertisement

 

Wadanda abin ya rutsa da su dai na dakon shiga jirgin kasa ne zuwa Warri da ke Jihar Delta a lokacin da maharan suka far musu.

Advertisement

Dakarun Rasha sun kakkaɓo wani jirgi maras matuƙi a garin Sevastopol na Ukraine

 

Kawo yanzu dai babu tabbas ko wani ya mutu a lamarin amma matafiyan da dama sun samu raunuka kamar yadda jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda a Edo, Chidi Nwabuzor, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Advertisement

 

Jami’in ya ce masu garkuwa da mutane dauke da bindigogi kirar AK 47, sun mamaye tashar jirgin ne da Yammacin ranar Asabar, inda suka rika harbi a iska kafin su yi awon gaba da matafiya da dama.

Advertisement

 

Harin na zuwa ne kasa da shekara guda bayan da ’yan ta’addan suka kaddamar da hari kan jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna inda suka kashe wasu fasinjojin jirgin tare da yin garkuwa da sama da 60 daga cikinsu.

Advertisement

 

Lamarin ya tilasta wa Gwamnatin Tarayya dakatar da sufurin jirgin kasa a hanyar Abuja zuwa Kaduna sama da watanni shida kafin maido da shi baya-bayan nan.

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending