Connect with us

News

Yan Bindiga Sun Sace Tsohon Shugaban NYSC da Wasu Mutane 

Published

on

Yan bindiga sun sace tsohon shugaban hukumar NYSC da wasu mutane a Katsina

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA  

Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da tsohon shugaban hukumar masu hidimtawa kasa (NYSC), Manjo Janar Mahraz Tsiga (mai ritaya), tare da wasu mutanen kauyen Tsiga da ke karamar hukumar Bakori a jihar Katsina.

Rahotanni sun bayyana cewa an sace mutanen ne a tsakar daren Laraba, duk da cewa hukumomi har yanzu ba su fitar da wata sanarwa ba dangane da lamarin.

Gobara Mai Muni Ta Lalata Kauyen Zago A Kano

Wata majiya ta shaidawa Prime Time cewa, tabbas tsohon shugaban hukumar NYSC yana cikin mutanen da aka yi garkuwa da su a kauyen Tsiga.

Har zuwa lokacin da ake rubuta wannan rahoto, babu wata sanarwa daga gwamnatin jihar Katsina ko rundunar ‘yan sanda dangane da sace mutanen.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending