Connect with us

News

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Yawaitar Hare-haren ’Yan Bindiga A Zamfara

Published

on

images 9 1 700x375

Mazauna akalla kauyuka 30 daga Dan-Isa da Kagara, a karamar hukumar Kaura-Namoda, Jihar Zamfara, sun gudanar da zanga-zanga a Gusau, babban birnin jihar, a ranar Alhamis, domin nuna damuwarsu kan tsanantar hare-haren ’yan bindiga a yankinsu.

Masu zanga-zangar – ciki har da mata da yara – sun isa harabar gidan gwamnatin jihar dauke da alluna da ke ɗauke da rubuce-rubuce irin su: “Muna bukatar zaman lafiya a kauyukan Kaura-Namoda,” “Gwamna Dauda Lawal da Matawalle, ku kawo mana dauki,” da “Ana kashe mu kowace rana.”

Advertisement

NAHCON Ta Sanar Da Naira Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Ajiya Na Aikin Hajjin 2026

Jagoran masu zanga-zangar, Lawal Kamilu daga Dan-Isa, ya ce dalilin fitowarsu shi ne nuna fushi da rashin amincewa da yadda hare-haren ke ci gaba da kashe mutane da yin garkuwa da su.

“Mun fito daga kauyuka kusan 30 saboda mafi yawan mutanenmu ko dai an kashe su, ko kuma ’yan bindiga sun yi garkuwa da su. Suna bukatar kudin fansa mai tarin yawa, alhali ba mu da abin da za mu bayar. Mun sayar da dukkan kadarorinmu da gonakanmu wajen biyan kudin fansar ’ya’yanmu da ’yan uwanmu da aka sace a baya,” in ji shi.

Advertisement

Masu zanga-zangar sun yi kira ga Ministan Tsaro, Bello Matawalle, da gwamnatin tarayya a karkashin shugabancin Bola Tinubu, da su gaggauta daukar mataki.

 

Advertisement

 

LEADSHIP

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending