Connect with us

News

An Sace Tsohon Sakataren Gwamnati A Inugu

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Yan bindiga sun sace tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Inugu, Dokta Dan Shere, tare da wasu matafiya da ba a tantace adadinsu ba.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne ranar Alhamis a hayar Enugu zuwa Ugwuogo, Nike zuwa Nsukka, a lokacin da Shere ke kan hanyarsa ta dawowa daga wani taro da ya halarta.

Advertisement

Babu barazanar tsaro a Abuja – IGP Usman Alkali

Majiyarmu ta ce ’yan bindigar wanda adadinsu ya kai takwas, sai da suka yi harbe-harben bindiga a iska don razana jama’a kafin daga bisani suka yi garkuwa da su.

Advertisement

Sace mutanen ya jefa jama’ar yankin cikin mummunan tashin hankali, inda suka yi kira ga jami’an tsaro da a gaggauta daukar matakin ceto su.

Shere ya yi Sakataren Gwmanatin jiahr ne a zamanin tsohon Gwamnan Inugu, Chimaroke Nnamani.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending