News
An Sace Tsohon Sakataren Gwamnati A Inugu
Yan bindiga sun sace tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Inugu, Dokta Dan Shere, tare da wasu matafiya da ba a tantace adadinsu ba.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne ranar Alhamis a hayar Enugu zuwa Ugwuogo, Nike zuwa Nsukka, a lokacin da Shere ke kan hanyarsa ta dawowa daga wani taro da ya halarta.
Babu barazanar tsaro a Abuja – IGP Usman Alkali
Majiyarmu ta ce ’yan bindigar wanda adadinsu ya kai takwas, sai da suka yi harbe-harben bindiga a iska don razana jama’a kafin daga bisani suka yi garkuwa da su.
Sace mutanen ya jefa jama’ar yankin cikin mummunan tashin hankali, inda suka yi kira ga jami’an tsaro da a gaggauta daukar matakin ceto su.
Shere ya yi Sakataren Gwmanatin jiahr ne a zamanin tsohon Gwamnan Inugu, Chimaroke Nnamani.
Advertisements
