Connect with us

News

Wata gobara ta lalata shaguna da dama tare da kashe mutum daya a babbar kasuwar Zamfara

Published

on

DAGA MUHAMMAD BASHIR MUSA

Wata gobara ta lalata shaguna da dama tare da kashe mutum daya a babbar kasuwar Gusau da ke jihar Zamfara.

Advertisement

Jaridar DAILY POST ta ruwaito cewa gobarar ta tashi ne da misalin karfe 8:30 na daren ranar Talata a bangaren kayan daki na babbar kasuwar jihar.

An yanke wa Imran Khan da matarsa hukuncin zaman gidan yari na shekara 14

A cewar kwamandan hukumar kashe gobara ta Najeriya, sabuwar ofishin kasuwa, Hamza Mohammed, wani mai shago wanda har yanzu ba a bayyana sunansa ba ya mutu a lokacin da yake kokarin shiga shagonsa domin kashe gobarar.

Advertisement

Jami’an kashe gobara na hukumar kashe gobara ta jihar sun yi ta fafatawa don hana gobarar  yaduwa zuwa wasu shaguna.

Duk da haka, shaguna da yawa abin ya shafa.

Advertisement

Kawo yanzu dai ba a san musabbabin tashin gobarar ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending