Connect with us

News

Yadda Hukumomi Ke Amfani Da Ƙarfin Iko Wajen Tauye Hakkokin Jama’a A Najeriya

Published

on

Ƙungiyoyin Fararen Hula Za Su Sake Fita Zanga Zangar Tsadar Rayuwa A Najeriya

A Najeriya, zalunci da tauye haƙƙin jama’a ba sabon abu ba ne, musamman idan wanda ke aikata hakan na da wani ƙarfin iko ko madafa ta gwamnati.

Yawanci idan an tauye wa mutum haƙƙinsa a Najeriya, ba a cika ganin ya tashi ya nemi ‘yancinsa ba, domin kuwa mafi yawan lokaci wanda ya zalunce shi na da ƙarfin da zai hana a tanka masa. Idan kuma hukuma ce, to kuwa lamarin yakan fi kamari.

Advertisement

DA DUMI-DUMI: Gobara Ta Tashi A Wani Otel Na Alhazan Najeriya A Makkah

Wani abu da ya dade yana jefa al’umma cikin kangin zalunci shi ne halin yin shiru ko nuna haƙuri a lokacin da aka cutar da mutum. Wannan hali ya jima yana zama hanya ga masu iko wajen cin zarafin jama’a babu mai ce musu uffan.

To amma alamu na nuna cewa yanzu mutane sun fara gajiya da yin shiru. Wasu na ganin cewa wannan shiru da haƙuri da aka dade ana yi ne ya sa hukumomi da wasu daidaikun mutane ke ci gaba da cutar da ‘yan kasa ba tare da fargabar sakamako ba.

Advertisement

A cewar wasu masu fashin baki, rashin tashi tsaye na al’umma wajen kare haƙƙinsu ne ke ba hukumomi damar ci karensu babu babbaka.

“Da zarar mutane sun daina yin shiru, kuma suka fara fitowa fili suna magana, komai na zalunci zai ragu,” in ji wani matashi da FRI HAUSA ta tattauna da shi.

Advertisement

Wasu na ganin cewa hanya mafi sauki ta kare haƙƙi da nuna rashin amincewa da cin zarafi ita ce zanga-zanga cikin lumana — hanyar da ke ba mutane damar bayyana damuwa ba tare da tada tarzoma ba.

Yanzu dai lokaci ya yi da jama’a za su fahimci cewa shiru ba mafita ba ne. Kare haƙƙin kai da na al’umma wajibi ne ga kowa da kowa.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending