Connect with us

News

IBADAN: Hausawa Sun Yi Zanga-zanga Kan Danganta Su Da Satar Mutane

Published

on

IMG 20260610 WA0075 (1)

Wasu daga cikin al’ummar Hausawa mazauna Ibadan, babban birnin Jihar Oyo, sun gudanar da zanga-zanga domin nuna rashin amincewarsu kan alaƙanta su da laifukan satar mutane da ke faruwa a jihar.

Masu zanga-zangar sun ce ba daidai ba ne a riƙa danganta dukkanin Hausawa da aikata laifuka saboda laifin wasu tsiraru.

Advertisement

Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida

Wannan zanga-zanga na zuwa ne makonni kaɗan bayan sace ɗalibai da malamai 46 a wani hari da aka kai makarantu uku a Ƙaramar Hukumar Oriire a jihar.

Advertisement

Al’ummar Hausawan sun buƙaci jama’a da hukumomi su guji yi musu kallon masu laifi saboda asalinsu ko ƙabilarsu, tare da jaddada cewa mafi yawan Hausawa mazauna jihar mutane ne masu zaman lafiya da bin doka.

 

Advertisement

 

 

Advertisement

AMINIYA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending