News
Gwamnatin Jahar Kano Zata Kaddamar Da Rabon Tallafin Rage Radadi Bayan Cire Tallafin Man Fetur

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
A yau ne gwamnatin jihar Kano za ta kaddamar da rabon kayan abinci a matsayin wani bangare na rage radadi, watanni uku bayan cire tallafin man Fetur da shugaban kasa a Bola Ahmad Tinubu ya yi.
Al’ummar Kano dai sun dade suna dakon matakan da za’a dauka na samar da saukin tsadar rayuwa, kuma a kwanakin baya wasu mata ma sun gudanar da zanga-zangar lumana suna neman a saukaka farashin abinci bayan da gwamnatin tarayya ta amince da Naira billiyan 5 ga kowace jiha.
Samar Da Asusun Sarrafa Shara A Kasar nan Zai Bunkasar Tattalin Arziki Da Inganta Muhalli – AWAMN
Sai dai a iya cewa jira ya kare a yanzu inda mai magana da yawun gwamna Abba Yusuf, Sanusi Bature ya tabbatar da safiyar yau a cikin wani gajeren sako da ya aike wa manema labarai cewa za a fara raba kayan abinci a yau.
Ya ce taron zai gudana ne a hukumar bunkasa aikin gonad a raya karkara ta Kano KNARDA da karfe 11 na safe ba tare da wani karin bayani ba.
